Skip to main content

Posts

Showing posts from August, 2022

ASALIN RUBUTUN HAUSAR BOKO KASHI Na ( 2 )

Zuriyar Harshen Hausa Masana ilimin harsuna sun karkasa harsunan duniya zuriya-zuriya. Kowane harshe na duniyar mutane dole da rukunin da yake. A rukunin da ya fito nan ake kirdadon tushensa da tushen masu magana da shi. Masana ilimin harshe sun ce: Hausa harshe ne daga cikin  zuriyar harsunan Chadi, waɗanda sun kai fiye da harsuna ɗari da ake magana da su a Arewacin Najeriya da Arewacin Kamaru da kuma tsakiyar Chadi.” Daga cikin harsuna iyalan Chadi, Hausa ta fi kowane bazuwa da yawan jama’a da karɓuwa da mamaye ƙasa. Daga cikin fahimtar sanin asalin harshe shi ne a san tarihinsa. Babban muhimmin abu shi ne gano dangantakar harshe da sauran harsunan da suke zuriya/iyali ɗaya. Babu makawa ga mai son sanin tushen Hausa ya yi ƙwaƙƙwaran nazarin harsuna iyalan Chadi. A tsarin ilimin harsuna an ce: Idan aka ce harshe (kaza) ɗan iyalan gungun harsuna (kaza) ne, ana son a tabbatar da cewa, a da can baya harshe ɗaya ne kacal daga gare shi ne sauran harsunan zuriyarsa suka tsir...

ASALIN RUBUTUN HAUSAR BOKO KASHI NA DAYA (1)

Rubuta Hausa a cikin bakaken boko ya samo asali ne tun wajen Karni na 17/18 lokacin da Turawan Mishan da ’yan kasuwa suka rika shigowa Nahiyar Afirka. Turawan sun yi kokarin sanin harshen Hausa da al’adunsa kamar yadda suka yi a kan sauran harsunan da suka tarar, inda suka rika aika rahotannin abin da suka samu zuwa kasashenmu don a rika bugawa a mujallu da littattfai. Kuma bincike ya nuna cewa an fara rubuta Hausa a cikin kalmomin boko ne a kasar Denmark a Karni na 18. Yadda aka fara rubutun Hausar Boko Sarkin Denmark na lokacin ne ya tura wakilansa zuwa kasashen Larabawa don su yi binciken kimiyya a 1773 Miladiyya, kuma a cikin wadanda ya tura akwai wani Bature mai suna B.G. Niebuhr. Bayan wannan bincike sai wani Balaraben kasar Tunisiya mai suna Abdurrahman da wani bawansa mutumin Borno da ya ji Hausa suka kai ziyayar jakadanci kasar Denmark. Niebuhr ya zama tafinta mai fassara tattaunawa a tsakanin Sarkin Denmark da Balaraben nan. Sai abota ta shiga tsakanin Niebuhr da ...

WAI ME YASA BAZAI SAKESU BA KAWAI YA HUTA?

A True Life Story! A garinmu Anyi wasu kishiyoyi guda biyu (2) masu bakaken zuciya, Babu ranar da garin Allah zai waye daga safiya zuwa maraice face Sai sunyi fada (Cacan Baki) ko Kuma dambe.  . In kuwa kaga haka bai faru ba, to tabbas dayace tayi tafiya ko Kuma rashin lafiya mai tsanani ya kwantar da ita. . Lamarin yana matukar damun Maigidansu, yayi duk wani abinda ya dace don ganin kawo karshen wannan badakalar amma kokarinsa bai kai ga matakin cin Nasara ba. . WAI ME YASA BAZAI SAKESU BA KAWAI YA HUTA? . Wannan shine abinda zaka ji bakunan mutane na furtawa a duk sanda aka tashi batu akan wannan al'amari. "Ni Kuwa cewa nayi: "Watakila yana saurara musu ne a dalilin 'ya'yansu.  . Toh amma menene amfanin hakan tunda su ba duba hakan suke yii ba. Sai dai a madadin duk wannan, Maigidan ya yankewa kansa wani hukunci Wanda yake gani shine daidai dashi, Wannan kuwa ba Komai bane illa daina zuwa gidansa a wasu lokuta na tsawon kwana biyu ko uku tare da cew...

TARIHIN ƊAN HAUSA (Sir Hanns Vischer)

WANENE HANNS VISCHER? Hanns Vischer shine baturen da ake masa lakabi da Dan Hausa, saboda kwarewarsa wajen magana da harshen. Ya shugabanci makarantar boko ta farko da aka samar a Arewacin Najeriya, kuma shi ya bukaci gwamnati ta samar da abubuwan karatu ga dalibai a wannan makaranta. A sakamakon haka an umarci wadansu malamai da su samar da litattafan Hausa, wadanda dalibai za su amfana da su. Ga misaalan litattafan da sunan wadanda suka wallafa su: (1) Iliya Dan Mai Karfi na Ahmad Ingawa. (2) Jiki Magayi na John Tafida da Rm East. (3) Shaihu Umar na Alhaji Abubakar Tafawa Balewa. (4) Ruwan Bagaja na Alhaji Abubakar Imam. Sir Hanns Vischer, CMG, CBE, haifaffen kasar Switzerland ne dan kasar Birtaniya wanda ya kasance mai ba da shawara kan harkokin ilimi ga gwamnatin Arewacin Najeriya Protectorate. An nada shi Daraktan Ilimi na farko na yankin Arewa kuma ya kirkiro manufofin farko na ilimin boko ga yankin. An haifi Ɗan Hausa a cikin shekarar 1876, bai fara aiki a ko ina ba ...

TARIHIN IBN TAYMIYYA ( RA ) تقي الدين أحمد بن عبد الحليم بن عبد السلام النميري الحراني)

Cikakken sunan Ibn Taimiyyah shine ' Taqiy al-Din 'Abu al-Abbas 'Ahmad ibn 'Abd al-Hallim ibn 'Abd as-Salam ibn ' Abdullah ibn al-Khiḍr ibn Muḥammad ibn al-Khiyr ibāllīr- ibn al-Khiḥr Ḥarrānī : أحمد بن عبد الحليم بن عبد السلام بن عبد الله بن الخضر بن محمد بن الخضر بن إبراهيم ب اللهن علي بن علي بن بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن علي بن عبد السلام . Sunan Ibn Taimiyyah ( ابن تيمية ) ba a saba ganinsa ba ya samo asali ne daga wata mace daga cikin iyalansa sabanin namiji, wanda al'ada ce ta da a lokacin kuma har yanzu. Lakabin " Taimiyya " ya fito ne daga kakarsa wacce ake kira Taimiyyah. Ta kasance mai nasiha kuma an yi masa lakabi da " Ibn Taimiyyah ". Taimiyya ta kasance fitacciyar mace, shahararriyar mai ilmi ta da takawa da sunan Ibn Taimiyya da yawa daga zuriyarta maza ne suka karba. Ibn Taimiyyah, sunan haihuwa Taqī ad-Dīn ʾAḥmad ibn 'Abd al-Hallim ibn 'Abd al-Salam al-Numayr...

Gembu Jihar Taraba Najeriya

Gembu birni ne, da ke a yankin Duwatsun Mambilla, a Jihar Taraba, a Nijeriya. Ita ce hedikwatar karamar hukumar Sardauna (tsohuwar "Mambilla") a jihar Taraba. Mutanen Mambilla ko Mambila na Najeriya suna zaune a tudun Mambilla. Kadan daga cikin 'yan ci-rani na Mambilla sun tashi daga duwatsun Mambilla zuwa filin Ndom da ke gefen Kamaru na kan iyakar kasa da kasa da kuma wasu kananan kauyuka, kamar sabuwar Namba, da ke kan arewa zuwa garuruwan Gashaka da Banyo. Mambila na Zaune a matsakaita tsayin kusan mita 1,348 (4,423 ft) sama da matakin teku,  yana daga cikin manyan biranen Najeriya. Tarihi An yi imani tun da dadewa cewa mutanen farko na mazaunan Duwatsun Mambilla su ne zuriyar kakannin Bantu. mutanen Bantu waɗanda suka zauna a Gembu ta zamani bayan faɗaɗar Bantu a faɗin Afirka daga 4000 zuwa 3500 Kafin Haihuwar Annabi Isa AS  Dalilin Da zai sanyaku zuwa mambila  1, Garin yafi ko'ina matan fulani kyawawa 2, Dutsen Mambila yana Jahar Taraba kuma shine wu...

Tarihin Sayyadina Umar bin Khaddab عمر بن الخطاب, (Allah Ya kara masa yarda):

Shimfiɗa.  Umar bn al-Khaṭṭāb ( RA) shi ne khalifan Rashidun na biyu, wanda ya yi mulki daga watan Agusta 634 har zuwa kashe shi a shekara ta 644. Ya gaji  Sayyidina Abubakar ( RA) a matsayin khalifan Rashidun na biyu a ranar 23 ga Agusta 634. Umar babban sahabi ne kuma surukinsa annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama. Menene Umar Ibn al-Khattab aka sani da shi? Umar babban sahabi ne kuma mashawarcin annabin musulunci Muhammad SAW, kuma ya zama shugaba musulmi na biyu bayan wafatin Muhammad ya kuma yi mulki na tsawon shekaru 10. Ya Musulunta a shekara ta 6 bayan wahayin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama na farko, ya shafe shekaru 18 yana sahabi Muhammad SAW.  “Da za a samu wani Annabi a bayana, da ya kasance Umar dan Khaddabi ne.”  – Manzon Allah (SAW). Shi ne Umar dan Khaddabi dan Nufailu dan Addi dan Abdul Uzza dan Ribalu dan Abdullahi dan Kurdu dan Razahu dan Addi dan Ka’abu, Bakuraishe, Bamakhzume. Sun hada nasaba da Annabi (SAW). Ana yi masa alku...

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNA TIN ANAN DUNIYA:-

 *1. Abubakar As-sidiq(R.A) *2. Umar Bin Khattab(R.A) *3. Uthman Bin Affan(R.A) *4. Aliyu Bin Abi-Talib(R.A) *5. Zubair Bin Auwam(R.) *6. Sa'adu Bin Abi Waqas(R.A) *7. Abu Ubaida Bin Jarrah(R.A) *8. Dalhatu Bin Ubaidullah(R.A) *9. Abdurrahman Bin Auf(R.A) *10. Sa'idu Bin Zaid Al-Quraishi(R.A). ♡♡♤♤♡♡♤♤♡♡ ALLAH YA BAMU ALBARKACINSU, ALLAH YA KARA LINKA RAHAMA DA YARDA A GARE SU AMEEEEEN.