Skip to main content

Gembu Jihar Taraba Najeriya

Gembu birni ne, da ke a yankin Duwatsun Mambilla, a Jihar Taraba, a Nijeriya. Ita ce hedikwatar karamar hukumar Sardauna (tsohuwar "Mambilla") a jihar Taraba.

Mutanen Mambilla ko Mambila na Najeriya suna zaune a tudun Mambilla. Kadan daga cikin 'yan ci-rani na Mambilla sun tashi daga duwatsun Mambilla zuwa filin Ndom da ke gefen Kamaru na kan iyakar kasa da kasa da kuma wasu kananan kauyuka, kamar sabuwar Namba, da ke kan arewa zuwa garuruwan Gashaka da Banyo.

Mambila na Zaune a matsakaita tsayin kusan mita 1,348 (4,423 ft) sama da matakin teku,  yana daga cikin manyan biranen Najeriya.

Tarihi

An yi imani tun da dadewa cewa mutanen farko na mazaunan Duwatsun Mambilla su ne zuriyar kakannin Bantu. mutanen Bantu waɗanda suka zauna a Gembu ta zamani bayan faɗaɗar Bantu a faɗin Afirka daga 4000 zuwa 3500 Kafin Haihuwar Annabi Isa AS 

Dalilin Da zai sanyaku zuwa mambila 

1, Garin yafi ko'ina matan fulani kyawawa

2, Dutsen Mambila yana Jahar Taraba kuma shine wuri mafi sanyi a Najeriya baki daya. Akasarin yara da ke tasowa a yankin ba su taɓa ganin na'urorin da ke bayar da sanyi a zahiri ba sai dai a talabijin ko kuma litattafai.

Gembu a ranar hudu ga watan Satumban shekarar 2021, yanayin sanyi ya kai maki 17 digiri selshiyos.

Shi ma shafin da ke wallafa bayanai na intanet Wikipedia ya tabbatar cewa ƙauyen Dorofi da ke kan tsaunin na Mambila shi ne yanki mafi sanyi a Najeriya.

Da zarar ka fara haurawa kan tsaunin daga wani ƙauye da ake kira Mayo Selbe da ke karamar hukumar Gashaka za ka hangi tsauni mai tudun gaske lulluɓe da koren ciyayi da bishiyoyi da hazon ƙanƙara iya hangenka.

Daga wannan ƙauyen ne yanayi ke sauyawa daga zafi zuwa sanyi ko kuma sanyi zuwa ɗan karen sanyi.

Kana isa kan tsaunin daga garin Maisamari har zuwa sauran ƙauyuka da suka yi iyaka da jamhuriyar Kamaru za ka iske kusan kowa ya yi shigar maganin sanyi.

Za ka ga mutane da manyan rigunan sanyi da ake kira "Kuntu" da hulunan sanyi da takalma sau ciki domin maganin sanyi.

3, Saboda  sanyi yasa mutanen wurin basa amfani da Firji, AC, ko fanka, domin duk wani nau'in kayan sha ko yaushe da sanyin sa. 

4, kusan Kowa a garin ya iya fillanci duk dacewa manyan yaruka da kabilu 4 ne a yankin wanda suka hada da Mambilawa, Fulani, Panso da Kakah. 

5, Hotel yanada araha a yankin domin akuwai dakin ₦1500

6, Garin yana da arzikin duwatsun daimond da blue sapaya, kana sunada arziƙin shanu shi yasa nama yake da araha a yankin. 

7, Sunada nau'in kayan itace da nau'in abinci daban-daban har da wanda baka taba ganiba balle ci, wanda suka hada da piya, ayaba, chanis apple, mangoro, bulumji, deppi, dankalin turawa, samaije da sauransu, gwaiba kam tun a hanya zaka tsaya ka tsinka a hanya. 

8, kauyukan da suke da kyawawan mata a dutsen mambila su hada da, Kakara, Leme, Yarimaru, Mayo-ndaga, Dorofi, Nguroje, da Galadima. 

9, Dutsen yafi ko ina yawan itacen zaiti a Najeriya 

10, Babu sauro a garin. 

11, Manyan garuruwa da suke kan dutsin mambila sun hada da, Gembu, Nguroje, Mayo-ndaga (dago cede) da Mai samari.

Comments

Popular posts from this blog

MAGANIN KARYA SIHIRI(HAYAKI)

 Alhamdulillah kamar yadda mukai Alkawarin zamu kawo maganin wanda yake karya sihiri ko jifa,ko sammu Allah ya nufa yau mun cika shi. Kuma shi wannan na hayaki ne wanda mutum zai hada ya rika zuba shi akan garwashi yana amfami dashi,yadda abun yake kuma shine..... ABINDA ZAA NEMA. 1. Kaikayi koma kan mashekiya 2. Garin kusdul hindi 3. Garin haltit Zaa hade wannan waje daya,sai a rika diban kadan ana zubawa akan wuta mara lafiya ya rika shakar hayakin. Idan kuma don kariya zaai kawai sai a saka a daki ko a cikin gida. Wallahu a'alamu Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati. LIKE AND SHARE.

ASALIN RUBUTUN HAUSAR BOKO KASHI Na ( 2 )

Zuriyar Harshen Hausa Masana ilimin harsuna sun karkasa harsunan duniya zuriya-zuriya. Kowane harshe na duniyar mutane dole da rukunin da yake. A rukunin da ya fito nan ake kirdadon tushensa da tushen masu magana da shi. Masana ilimin harshe sun ce: Hausa harshe ne daga cikin  zuriyar harsunan Chadi, waɗanda sun kai fiye da harsuna ɗari da ake magana da su a Arewacin Najeriya da Arewacin Kamaru da kuma tsakiyar Chadi.” Daga cikin harsuna iyalan Chadi, Hausa ta fi kowane bazuwa da yawan jama’a da karɓuwa da mamaye ƙasa. Daga cikin fahimtar sanin asalin harshe shi ne a san tarihinsa. Babban muhimmin abu shi ne gano dangantakar harshe da sauran harsunan da suke zuriya/iyali ɗaya. Babu makawa ga mai son sanin tushen Hausa ya yi ƙwaƙƙwaran nazarin harsuna iyalan Chadi. A tsarin ilimin harsuna an ce: Idan aka ce harshe (kaza) ɗan iyalan gungun harsuna (kaza) ne, ana son a tabbatar da cewa, a da can baya harshe ɗaya ne kacal daga gare shi ne sauran harsunan zuriyarsa suka tsir...

Tarihin Sayyadina Umar bin Khaddab عمر بن الخطاب, (Allah Ya kara masa yarda):

Shimfiɗa.  Umar bn al-Khaṭṭāb ( RA) shi ne khalifan Rashidun na biyu, wanda ya yi mulki daga watan Agusta 634 har zuwa kashe shi a shekara ta 644. Ya gaji  Sayyidina Abubakar ( RA) a matsayin khalifan Rashidun na biyu a ranar 23 ga Agusta 634. Umar babban sahabi ne kuma surukinsa annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama. Menene Umar Ibn al-Khattab aka sani da shi? Umar babban sahabi ne kuma mashawarcin annabin musulunci Muhammad SAW, kuma ya zama shugaba musulmi na biyu bayan wafatin Muhammad ya kuma yi mulki na tsawon shekaru 10. Ya Musulunta a shekara ta 6 bayan wahayin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama na farko, ya shafe shekaru 18 yana sahabi Muhammad SAW.  “Da za a samu wani Annabi a bayana, da ya kasance Umar dan Khaddabi ne.”  – Manzon Allah (SAW). Shi ne Umar dan Khaddabi dan Nufailu dan Addi dan Abdul Uzza dan Ribalu dan Abdullahi dan Kurdu dan Razahu dan Addi dan Ka’abu, Bakuraishe, Bamakhzume. Sun hada nasaba da Annabi (SAW). Ana yi masa alku...