Skip to main content

WAI ME YASA BAZAI SAKESU BA KAWAI YA HUTA?

A True Life Story!

A garinmu Anyi wasu kishiyoyi guda biyu (2) masu bakaken zuciya, Babu ranar da garin Allah zai waye daga safiya zuwa maraice face Sai sunyi fada (Cacan Baki) ko Kuma dambe. 
.
In kuwa kaga haka bai faru ba, to tabbas dayace tayi tafiya ko Kuma rashin lafiya mai tsanani ya kwantar da ita.
.
Lamarin yana matukar damun Maigidansu, yayi duk wani abinda ya dace don ganin kawo karshen wannan badakalar amma kokarinsa bai kai ga matakin cin Nasara ba.
.
WAI ME YASA BAZAI SAKESU BA KAWAI YA HUTA?
.
Wannan shine abinda zaka ji bakunan mutane na furtawa a duk sanda aka tashi batu akan wannan al'amari.
"Ni Kuwa cewa nayi: "Watakila yana saurara musu ne a dalilin 'ya'yansu. 
.
Toh amma menene amfanin hakan tunda su ba duba hakan suke yii ba.

Sai dai a madadin duk wannan, Maigidan ya yankewa kansa wani hukunci Wanda yake gani shine daidai dashi, Wannan kuwa ba Komai bane illa daina zuwa gidansa a wasu lokuta na tsawon kwana biyu ko uku tare da cewar yana gari, ba tafiya yayi ba. 
.
Wanda hakan kamar kuntatuwane a gareshi,
Ana cikin hakanne, rannan Sai amarya ta zabura kamar wadda aka yiwa allurar soja. 
.
Bayan uwar gidanta ta gama abincin dare tana shirye shiryen kintsawa domin dawowan Maigida, Ashe Amarya ta dafa ruwa a stove mai shegen zafi, ta dibi gishiri mai yawa ta afka cikin ruwan zafinnan.
.
Koda uwar gida ta shiga bandaki (Bath room) domin ta yi wanka, can kuwa Sai amarya tabi bayanta, tana shiga Sai ta tarar da 'yar uwar tata (Uwar Gida) a tube harma ta goga sabulu a fuska. 
.
Cikin rashin Imani, haka amaryarnan ta Daga ruwan zafi da ta tafi dashi (Wanda yake hade da gishiri) ta kwarawa uwar gidanta a jiki!
.
Uwar gidannan Ta saka salati gami da yin wata kara (Ihu) mai zaburarwa. 
.
Kafin kace kobo jama'a sun taru a gidan, Ita kuwa amaryar da taga haka Sai ta ari Na kare.
.
Nan da nan aka sungumi uwar gidannan zuwa asibiti, idan ka ganta ba zaka so ka Kuma ganinta ba "domin ilahirin fatar (skin) jikinta ya salube.
.
Ya dauketa adadin awowi mai yawan gaske kafin ta farfado, kamar yadda ya dauketa adadin watanni mai yawan gaske kafin ta warke. Koda ta warke, haka kamanninta gaba daya ya chanja. Abindai Sai Wanda ya gani.
.
Nasan mai karatu ya zaku yaji ko wani irin mataki Mijin ya dauka akan amaryar, to ba Komai yayi mata ba illa iyaka ya saketa shika uku. 
.
Su Kuma iyayen uwar Gida suka ce basu yarda ba Sai anje kotu, amma daga bisani da aka zauna a Gida Sai aka fahimci juna, aka sasanta Kuma aka yafi juna.

Allah ya rabamu da irin wadannan mata, su Kuma Allah ya sauwake musu, Ameen.

Comments

Popular posts from this blog

MAGANIN KARYA SIHIRI(HAYAKI)

 Alhamdulillah kamar yadda mukai Alkawarin zamu kawo maganin wanda yake karya sihiri ko jifa,ko sammu Allah ya nufa yau mun cika shi. Kuma shi wannan na hayaki ne wanda mutum zai hada ya rika zuba shi akan garwashi yana amfami dashi,yadda abun yake kuma shine..... ABINDA ZAA NEMA. 1. Kaikayi koma kan mashekiya 2. Garin kusdul hindi 3. Garin haltit Zaa hade wannan waje daya,sai a rika diban kadan ana zubawa akan wuta mara lafiya ya rika shakar hayakin. Idan kuma don kariya zaai kawai sai a saka a daki ko a cikin gida. Wallahu a'alamu Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati. LIKE AND SHARE.

Tarihin Sayyadina Umar bin Khaddab عمر بن الخطاب, (Allah Ya kara masa yarda):

Shimfiɗa.  Umar bn al-Khaṭṭāb ( RA) shi ne khalifan Rashidun na biyu, wanda ya yi mulki daga watan Agusta 634 har zuwa kashe shi a shekara ta 644. Ya gaji  Sayyidina Abubakar ( RA) a matsayin khalifan Rashidun na biyu a ranar 23 ga Agusta 634. Umar babban sahabi ne kuma surukinsa annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama. Menene Umar Ibn al-Khattab aka sani da shi? Umar babban sahabi ne kuma mashawarcin annabin musulunci Muhammad SAW, kuma ya zama shugaba musulmi na biyu bayan wafatin Muhammad ya kuma yi mulki na tsawon shekaru 10. Ya Musulunta a shekara ta 6 bayan wahayin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama na farko, ya shafe shekaru 18 yana sahabi Muhammad SAW.  “Da za a samu wani Annabi a bayana, da ya kasance Umar dan Khaddabi ne.”  – Manzon Allah (SAW). Shi ne Umar dan Khaddabi dan Nufailu dan Addi dan Abdul Uzza dan Ribalu dan Abdullahi dan Kurdu dan Razahu dan Addi dan Ka’abu, Bakuraishe, Bamakhzume. Sun hada nasaba da Annabi (SAW). Ana yi masa alku...

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNA TIN ANAN DUNIYA:-

 *1. Abubakar As-sidiq(R.A) *2. Umar Bin Khattab(R.A) *3. Uthman Bin Affan(R.A) *4. Aliyu Bin Abi-Talib(R.A) *5. Zubair Bin Auwam(R.) *6. Sa'adu Bin Abi Waqas(R.A) *7. Abu Ubaida Bin Jarrah(R.A) *8. Dalhatu Bin Ubaidullah(R.A) *9. Abdurrahman Bin Auf(R.A) *10. Sa'idu Bin Zaid Al-Quraishi(R.A). ♡♡♤♤♡♡♤♤♡♡ ALLAH YA BAMU ALBARKACINSU, ALLAH YA KARA LINKA RAHAMA DA YARDA A GARE SU AMEEEEEN.