Skip to main content

WAI ME YASA BAZAI SAKESU BA KAWAI YA HUTA?

A True Life Story!

A garinmu Anyi wasu kishiyoyi guda biyu (2) masu bakaken zuciya, Babu ranar da garin Allah zai waye daga safiya zuwa maraice face Sai sunyi fada (Cacan Baki) ko Kuma dambe. 
.
In kuwa kaga haka bai faru ba, to tabbas dayace tayi tafiya ko Kuma rashin lafiya mai tsanani ya kwantar da ita.
.
Lamarin yana matukar damun Maigidansu, yayi duk wani abinda ya dace don ganin kawo karshen wannan badakalar amma kokarinsa bai kai ga matakin cin Nasara ba.
.
WAI ME YASA BAZAI SAKESU BA KAWAI YA HUTA?
.
Wannan shine abinda zaka ji bakunan mutane na furtawa a duk sanda aka tashi batu akan wannan al'amari.
"Ni Kuwa cewa nayi: "Watakila yana saurara musu ne a dalilin 'ya'yansu. 
.
Toh amma menene amfanin hakan tunda su ba duba hakan suke yii ba.

Sai dai a madadin duk wannan, Maigidan ya yankewa kansa wani hukunci Wanda yake gani shine daidai dashi, Wannan kuwa ba Komai bane illa daina zuwa gidansa a wasu lokuta na tsawon kwana biyu ko uku tare da cewar yana gari, ba tafiya yayi ba. 
.
Wanda hakan kamar kuntatuwane a gareshi,
Ana cikin hakanne, rannan Sai amarya ta zabura kamar wadda aka yiwa allurar soja. 
.
Bayan uwar gidanta ta gama abincin dare tana shirye shiryen kintsawa domin dawowan Maigida, Ashe Amarya ta dafa ruwa a stove mai shegen zafi, ta dibi gishiri mai yawa ta afka cikin ruwan zafinnan.
.
Koda uwar gida ta shiga bandaki (Bath room) domin ta yi wanka, can kuwa Sai amarya tabi bayanta, tana shiga Sai ta tarar da 'yar uwar tata (Uwar Gida) a tube harma ta goga sabulu a fuska. 
.
Cikin rashin Imani, haka amaryarnan ta Daga ruwan zafi da ta tafi dashi (Wanda yake hade da gishiri) ta kwarawa uwar gidanta a jiki!
.
Uwar gidannan Ta saka salati gami da yin wata kara (Ihu) mai zaburarwa. 
.
Kafin kace kobo jama'a sun taru a gidan, Ita kuwa amaryar da taga haka Sai ta ari Na kare.
.
Nan da nan aka sungumi uwar gidannan zuwa asibiti, idan ka ganta ba zaka so ka Kuma ganinta ba "domin ilahirin fatar (skin) jikinta ya salube.
.
Ya dauketa adadin awowi mai yawan gaske kafin ta farfado, kamar yadda ya dauketa adadin watanni mai yawan gaske kafin ta warke. Koda ta warke, haka kamanninta gaba daya ya chanja. Abindai Sai Wanda ya gani.
.
Nasan mai karatu ya zaku yaji ko wani irin mataki Mijin ya dauka akan amaryar, to ba Komai yayi mata ba illa iyaka ya saketa shika uku. 
.
Su Kuma iyayen uwar Gida suka ce basu yarda ba Sai anje kotu, amma daga bisani da aka zauna a Gida Sai aka fahimci juna, aka sasanta Kuma aka yafi juna.

Allah ya rabamu da irin wadannan mata, su Kuma Allah ya sauwake musu, Ameen.

Comments

Popular posts from this blog

MAGANIN KARYA SIHIRI(HAYAKI)

 Alhamdulillah kamar yadda mukai Alkawarin zamu kawo maganin wanda yake karya sihiri ko jifa,ko sammu Allah ya nufa yau mun cika shi. Kuma shi wannan na hayaki ne wanda mutum zai hada ya rika zuba shi akan garwashi yana amfami dashi,yadda abun yake kuma shine..... ABINDA ZAA NEMA. 1. Kaikayi koma kan mashekiya 2. Garin kusdul hindi 3. Garin haltit Zaa hade wannan waje daya,sai a rika diban kadan ana zubawa akan wuta mara lafiya ya rika shakar hayakin. Idan kuma don kariya zaai kawai sai a saka a daki ko a cikin gida. Wallahu a'alamu Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati. LIKE AND SHARE.

ASALIN RUBUTUN HAUSAR BOKO KASHI Na ( 2 )

Zuriyar Harshen Hausa Masana ilimin harsuna sun karkasa harsunan duniya zuriya-zuriya. Kowane harshe na duniyar mutane dole da rukunin da yake. A rukunin da ya fito nan ake kirdadon tushensa da tushen masu magana da shi. Masana ilimin harshe sun ce: Hausa harshe ne daga cikin  zuriyar harsunan Chadi, waɗanda sun kai fiye da harsuna ɗari da ake magana da su a Arewacin Najeriya da Arewacin Kamaru da kuma tsakiyar Chadi.” Daga cikin harsuna iyalan Chadi, Hausa ta fi kowane bazuwa da yawan jama’a da karɓuwa da mamaye ƙasa. Daga cikin fahimtar sanin asalin harshe shi ne a san tarihinsa. Babban muhimmin abu shi ne gano dangantakar harshe da sauran harsunan da suke zuriya/iyali ɗaya. Babu makawa ga mai son sanin tushen Hausa ya yi ƙwaƙƙwaran nazarin harsuna iyalan Chadi. A tsarin ilimin harsuna an ce: Idan aka ce harshe (kaza) ɗan iyalan gungun harsuna (kaza) ne, ana son a tabbatar da cewa, a da can baya harshe ɗaya ne kacal daga gare shi ne sauran harsunan zuriyarsa suka tsir...

MARIGAYA SHAIKH JA'AFAR DA SHAIKH ALBANI ZARIA

A kullum ana samun Guluwwi ne a inda jahilci ya hadu da zafin kai da wautar tunani. Wannan ya sa za ka samu wadannan abubuwa su ne sababi na Guluwwi a Kafirtawa da Guluwwi a Bidi'antarwa. A cikin kwanakin nan ana tattauna wasu sababbin maganganu da suka bayyana na wani daga cikin 'Yan Kungiyar Salafiyyun masu Guluwwi a Bidi'antarwa na bidi'antar da Marigayi Shaikh Ja'afar da Shaikh Albani Zari'a, da kuma wasu Malaman da a yanzu suna da rai. Alhali in ka nazarci hukuncin da wadannan 'Yan Kungiyar Salafiyyun din suka yi ga wadannan Malamai za ka ga kawai ya ginu ne a kan jahilci da zafin kai. Dalili a kan haka, matasan sun jahilci sabuban Bidi'a, da halin da ake bidi'antarwa, da yanayin mutumin da ake bidi'antarwa. Saboda ba kowane wanda aka samu wata dabi'a ta 'Yan Bidi'a a tare da shi yake zama Dan Bidi'a ba. Za ka iya samun mutum da wata dabi'a ta Khawarijawa amma kuma bai zama Bakhawarije ba. Shaikhul Islami ya ce:...