Skip to main content

SHIN KASAN BABU ABIN DA YAKE KAWO SABANI NA RABUWAR KAI KAMAR JAHILCI DA ZALUNCI DA MUMMUNAN NUFI

Lallai sabuba da dalilai da suke kaiwa ga mummunan sabani wanda Allah da Manzonsa (saw) suka yi zargi a kansa, kuma Allah ya tanadi azaba a kansa, wanda yake raba kan al'umma suna da yawa, amma mafi girmansu shi ne JAHILCI da BACIN NIYYA DA MUNGUN NUFI, wanda ya kunshi kulla zalunci da hasada a cikin zuciya da son neman daukaka a bayan kasa. Wannan shi ne sababin da ya sa Yahudawa suka yi sabani da rarrabuwa a tsakaninsu, kuma Allah ya zargesu a dalilin haka.
Allah ya ce:
ولقد آتينا بني إسرائيل الكتاب والحكم والنبوة ورزقناهم من الطيبات وفضلناهم على العالمين (16) وآتيناهم بينات من الأمر فما اختلفوا إلا من بعد ما جاءهم العلم بغيا بينهم إن ربك يقضي بينهم يوم القيامة فيما كانوا فيه يختلفون (17)

Shaikhul Islam Ibnu Taimiyyah (r) ya ce:
الاختلاف المذموم من الطرفين يكون سببه تارة: فساد النية؛ لما في النفوس من البغي والحسد وإرادة العلو في الأرض ونحو ذلك، فيحب لذلك ذم قول غيرها، أو فعله، أو غلبته ليتميز عليه، أو يحب قول من يوافقه في نسب أو مذهب أو بلد أو صداقة، ونحو ذلك، لما في قيام قوله من حصول الشرف والرئاسة وما أكثر هذا من بني آدم، وهذا ظلم.
ويكون سببه - تارة - جهل المختلفين بحقيقة الأمر الذي يتنازعان فيه، أو الجهل بالدليل الذي يرشد به أحدهما الآخر، أو جهل أحدهما بما مع الآخر من الحق: في الحكم، أو في الدليل، وإن كان عالما بما مع نفسه من الحق حكما ودليلا.
والجهل والظلم: هما أصل كل شر، كما قال سبحانه: {وحملها الإنسان إنه كان ظلوما جهولا}.

Ya ce:
"Mummunan sabani (na rabuwar kai) wanda yake abin zargi a tsakanin dukkan bangarorin guda 2, a wani lokacin sababinsa yana kasancewa ne a dalilin bacin niyya (mummunan nufi), saboda abin da ke cikin zukata na zalunci (wuce iyaka da ketare haddin Shari'a ta hanyar kin aikata wani abin da aka wajabta a lokacin sabanin ko aikata wani abin da aka haramta in sabanin ya auku), da hasada da son samun daukaka a bayan kasa da makamancin haka. Saboda wannan sai bangare ya so ya zargi ra'ayin daya bangaren, ko aikinsa, ya ki yarda da shi, ko neman ya yi galba a kansa don ya nuna ya fi shi, ko ya so ra'ayin wanda ya dace da shi a dangantaka ko mazhaba ko gari ko abokantaka da makamancin haka, saboda in ra'ayinsa ya tabbata ya tsayu to zai samu matsayi da shugabanci. Abin mamaki, akwai irin wannan kuwa masu yawa a cikin 'yan adam. Wannan kuwa zalunci ne (wuce iyakan Allah).
A wani lokacin kuwa sababin sabanin bangarorin yana kasancewa ne a dalilin jahilcin masu sabanin ne a kan hakikanin lamarin da suke sabani a kansa, ko jahilci game da dalilin da daya bangaren yake kafa hujja da shi ma daya bangaren, ko jahilcin daya bangaren da dalilin da yake tare da daya bangaren na gaskiya, a hukuncin ko a dalilin (imma yana da gaskiya a hukunci, amma ba shi da gaskiya a dalili, ko kuma yana da gaskiya a dalili amma kuma ba shi da gaskiya a hukunci), ko da kuwa shi yana da ilmi game da abin da ya rike nasa na gaskiya a hukuncin da dalilin.
JAHILCI DA ZALUNCI SU NE ASALIN KOWANE SHARRI, kamar yadda Allah ya ce:
{وحملها الإنسان إنه كان ظلوما جهولا}
"... Mutum ya kasance mai matukar zalunci da jahilci".

Duba Iqtidha'us Siradil Mustaqeem 1/ 131 - 132.

Abin lura:
1. Babban abin da yake haifar da rabuwar kai a cikin al'umma shi ne ZALUNCI DA JAHILCI.
2. Zalunci shi ne ketare iyakan Allah da dokokin Shari'arsa, ta hanyar kin aikata abin da ya wajaba a lokacin da sabani ya faru, ko aikata abin da ya haramta. Kamar kin yarda da SULHU, ko kin yarda da ZAMA TARE DON A TATTAUNA MAS'ALOLIN DA AKA YI SABANI A KANSU, ko KAURACE MA JUNA, ko KIN YIN SALLAMA DA YANKE ALAKA A TSAKANI, ko KIN KARBAN GASKIYA BAYAN TA BAYYANA da makamancin irin abubuwan da suke wajibi ne a aikatasu a lokacin da sabani ya auku a tsakanin bangarori guda biyu na Ahlus Sunna ko suka haramta a aikatasu.
3. Jahilci imma ya zama ta bangaren malamai, ko ta bangaren mabiya.
(a) Ta bangaren malamai shi ne wanda yake kasancewa a sakamakon gazawa wajen bincike a kan mas'alolin da aka yi sabani a kansu, ta yadda zai jahilci hakikanin mas'alolin a dalili ko a hukunci, ko ya jahilci na abokin sabanin nasa.
(b) Ta bangaren mabiya kuwa, a mafi yawan hali za ka samu mabiyan su mukallidai ne, ba su da ta cewa a mas'alolin ilmi, amma kuma su ne a kan gaba wajen zalunci da rura wutar fitina da haddasa gaba da kiyayya a tsakani, har su taimaka wa malamin nasu ko jagoran nasu wajen kin yarda da gaskiya bayan ta bayyana masa. Irin wadannan mabiya sun zama shedanu, masu haddasa fitina da raba kan al'umma, masu toshe hanyar Allah.
4. Mummunan nufi shi yake haifar da ta'assubanci (bin ra'ayi don biyan bukata ta kashin kai ko son zuciya) da kin karban gaskiya da aiki da ita.
5. Duka wadannan ababen tambaya ne a ranar kiyama, Allah ya yi gargadi a kan sabani na rabuwar kai da sabubansu, kuma ya tanadi azaba mai girma a kansu.

Ya Allah ka yi mana afuwa ka kubutar da mu.

Comments

Popular posts from this blog

MAGANIN KARYA SIHIRI(HAYAKI)

 Alhamdulillah kamar yadda mukai Alkawarin zamu kawo maganin wanda yake karya sihiri ko jifa,ko sammu Allah ya nufa yau mun cika shi. Kuma shi wannan na hayaki ne wanda mutum zai hada ya rika zuba shi akan garwashi yana amfami dashi,yadda abun yake kuma shine..... ABINDA ZAA NEMA. 1. Kaikayi koma kan mashekiya 2. Garin kusdul hindi 3. Garin haltit Zaa hade wannan waje daya,sai a rika diban kadan ana zubawa akan wuta mara lafiya ya rika shakar hayakin. Idan kuma don kariya zaai kawai sai a saka a daki ko a cikin gida. Wallahu a'alamu Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati. LIKE AND SHARE.

Tarihin Sayyadina Umar bin Khaddab عمر بن الخطاب, (Allah Ya kara masa yarda):

Shimfiɗa.  Umar bn al-Khaṭṭāb ( RA) shi ne khalifan Rashidun na biyu, wanda ya yi mulki daga watan Agusta 634 har zuwa kashe shi a shekara ta 644. Ya gaji  Sayyidina Abubakar ( RA) a matsayin khalifan Rashidun na biyu a ranar 23 ga Agusta 634. Umar babban sahabi ne kuma surukinsa annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama. Menene Umar Ibn al-Khattab aka sani da shi? Umar babban sahabi ne kuma mashawarcin annabin musulunci Muhammad SAW, kuma ya zama shugaba musulmi na biyu bayan wafatin Muhammad ya kuma yi mulki na tsawon shekaru 10. Ya Musulunta a shekara ta 6 bayan wahayin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama na farko, ya shafe shekaru 18 yana sahabi Muhammad SAW.  “Da za a samu wani Annabi a bayana, da ya kasance Umar dan Khaddabi ne.”  – Manzon Allah (SAW). Shi ne Umar dan Khaddabi dan Nufailu dan Addi dan Abdul Uzza dan Ribalu dan Abdullahi dan Kurdu dan Razahu dan Addi dan Ka’abu, Bakuraishe, Bamakhzume. Sun hada nasaba da Annabi (SAW). Ana yi masa alku...

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNA TIN ANAN DUNIYA:-

 *1. Abubakar As-sidiq(R.A) *2. Umar Bin Khattab(R.A) *3. Uthman Bin Affan(R.A) *4. Aliyu Bin Abi-Talib(R.A) *5. Zubair Bin Auwam(R.) *6. Sa'adu Bin Abi Waqas(R.A) *7. Abu Ubaida Bin Jarrah(R.A) *8. Dalhatu Bin Ubaidullah(R.A) *9. Abdurrahman Bin Auf(R.A) *10. Sa'idu Bin Zaid Al-Quraishi(R.A). ♡♡♤♤♡♡♤♤♡♡ ALLAH YA BAMU ALBARKACINSU, ALLAH YA KARA LINKA RAHAMA DA YARDA A GARE SU AMEEEEEN.