Skip to main content

Yadda Ake Yin Sallar Jana'iza



'YAN-UWA mafi yawancinmu, muna yin Sallar Jana'iza amma kuma ba mu san abinda ake fada a cikin kowacce Kabbara ba.
Dan haka ya sa muka ga cewa
yana da kyau mu ware wani lokaci na musamman, Domin fahimtar
da mu yadda ake yin sallar Jana'za.

'YAN-UWA ita dai Sallar janai'za, tana da babban lada, ga wanda ya aikata
ta kamar yadda Manzon Allah (SAW) ya koyar, dan haka yana da kyau, mu tsaya mu koya.

Kamar yadda na ce, sallar jana'za tana da kabbarori guda hudu ne
kawai kuma kowacce Kabbara da abin da ake fada a cikinta.

1. KABBARA TA FARKO ana karanta {suraul-fatiha} ne kawai, banda wata sura, ko wata a'ya.

2. KABBARA TA BIYU ana karanta Salatin Annabi ba wani salati na daban ba.

3. KABBARA TA UKU ana yin addu'a ga wanda ya mutu mace ko namiji.

4. KABBARA TA HUDU za ka yi addu'a ne ga sauran al'ummar Musulmi Wadanda suke Raye da matattu.

DAN UWA KANA GAMAWA sai ka jira Liman ya yi sallama.
Ita kuma sallamar guda daya ce tak! Kuma za ka yi ta ne a bangaren damanka.

Allah muke roko da ya kara tabbatar damu akan Sunnar Annabin Rahama, Manzon Allah (S.A.W).

Akwai bukatar a yada Wan nan Sako Dan Allah ta Hanyar Share. domin 'yan uwa musulmai su karu. Allah yabada ikon Hakan Ameen

Comments

Popular posts from this blog

Tarihin Sayyadina Umar bin Khaddab عمر بن الخطاب, (Allah Ya kara masa yarda):

Shimfiɗa.  Umar bn al-Khaṭṭāb ( RA) shi ne khalifan Rashidun na biyu, wanda ya yi mulki daga watan Agusta 634 har zuwa kashe shi a shekara ta 644. Ya gaji  Sayyidina Abubakar ( RA) a matsayin khalifan Rashidun na biyu a ranar 23 ga Agusta 634. Umar babban sahabi ne kuma surukinsa annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama. Menene Umar Ibn al-Khattab aka sani da shi? Umar babban sahabi ne kuma mashawarcin annabin musulunci Muhammad SAW, kuma ya zama shugaba musulmi na biyu bayan wafatin Muhammad ya kuma yi mulki na tsawon shekaru 10. Ya Musulunta a shekara ta 6 bayan wahayin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama na farko, ya shafe shekaru 18 yana sahabi Muhammad SAW.  “Da za a samu wani Annabi a bayana, da ya kasance Umar dan Khaddabi ne.”  – Manzon Allah (SAW). Shi ne Umar dan Khaddabi dan Nufailu dan Addi dan Abdul Uzza dan Ribalu dan Abdullahi dan Kurdu dan Razahu dan Addi dan Ka’abu, Bakuraishe, Bamakhzume. Sun hada nasaba da Annabi (SAW). Ana yi masa alku...

MAGANIN KARYA SIHIRI(HAYAKI)

 Alhamdulillah kamar yadda mukai Alkawarin zamu kawo maganin wanda yake karya sihiri ko jifa,ko sammu Allah ya nufa yau mun cika shi. Kuma shi wannan na hayaki ne wanda mutum zai hada ya rika zuba shi akan garwashi yana amfami dashi,yadda abun yake kuma shine..... ABINDA ZAA NEMA. 1. Kaikayi koma kan mashekiya 2. Garin kusdul hindi 3. Garin haltit Zaa hade wannan waje daya,sai a rika diban kadan ana zubawa akan wuta mara lafiya ya rika shakar hayakin. Idan kuma don kariya zaai kawai sai a saka a daki ko a cikin gida. Wallahu a'alamu Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati. LIKE AND SHARE.

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNA TIN ANAN DUNIYA:-

 *1. Abubakar As-sidiq(R.A) *2. Umar Bin Khattab(R.A) *3. Uthman Bin Affan(R.A) *4. Aliyu Bin Abi-Talib(R.A) *5. Zubair Bin Auwam(R.) *6. Sa'adu Bin Abi Waqas(R.A) *7. Abu Ubaida Bin Jarrah(R.A) *8. Dalhatu Bin Ubaidullah(R.A) *9. Abdurrahman Bin Auf(R.A) *10. Sa'idu Bin Zaid Al-Quraishi(R.A). ♡♡♤♤♡♡♤♤♡♡ ALLAH YA BAMU ALBARKACINSU, ALLAH YA KARA LINKA RAHAMA DA YARDA A GARE SU AMEEEEEN.