Skip to main content

USULUS SALAFIYYA

Usulus Salafiyya su ne tushe da ginshikan da Salafiyya ta hakika ta ginu a kansu. Kuma kowane asali za ka samu dalili a kansa karara a cikin Alkur'ani ko Sunnar Manzon Allah (saw), kuma Salaf Magaba suka yi Ijma'i a kansa.

Wadannan ginshikai kuwa su ne kamar haka:
(1) Bin Alkur'ani da Sunna da girmama su da sallama musu, da daukar Addini daga gare su.
(2) Riko da fahimtar Salaf Magabata da bin Ijma'insu.
  • (3) Yin imani da Rakunnan Imani guda shida:
a) Babban tushensu shi ne Imani da Allah, ta hanyar kadaita shi a Rububiyyarsa, da kadaita shi a bauta, da tabbatar da Sunayensa da Siffofinsa da suka zo cikin Alkur'ani da Sunna, ba tare da Tawili ko kamantawa ko korewa ba.
b) Imani da Mala'ikun Allah, da Littatafansa, da Manzanninsa, da Ranar karshe.
c) Imani da Kaddara na alherinsa da na sharrinsa.
(4) Imani magana ne da aiki, yana karuwa, yana raguwa da aikata sabo.
(5) Nisantar kafirta Musulmi a kan aikata sabo, sai dai in ya aikata abin da yake warware Muslunci.
(6) Sauraro da da'a ma shugabannin Musulmai ko da azzalumai ne, matukar ba su yi umurni da sabon Allah ba.
(7) Rashin yin tawaye wa shugabannin Musulmai idan sun aikata sabo matukar bai kai matsayin kafirci ba.
(8) Girmama Sahabbai, da ganin falalarsu da wanke zuciya da tsare harshe a kansu, da yi musu addu'a ta samun yardar Allah.
(9) Son Alul Baiti da Matan Annabi (saw) da jibintarsu da ganin falalarsu.
(10) Haduwa a kan Bin Sunna da nesantar rarrabuwa.
(11) Nesantar Bidi'a da 'Yan Bidi'a.

Wadannan ginshikai, manyan Malaman Sunna sun tabbaar da su cikin littatafansu, musamman:
1- Usulus Sunna, da aka ruwaito daga Imamu Ahmad bn Hanbal.
2- Al-Aqidatut Dahawiyya, na Imamu Dahawiy.
3- Al-Aqidatul Wasidiyyah, na Shaikhul Islami Ibn Taimiyya.

Don haka, duk wani abu da babu shi karara a cikin Alkur'ani da Sunna, kuma ba ya cikin wadannan littatafai guda uku da muka ambata, to babu yadda za a yi ya zama Asali daga cikin "Usulus Salafiyya ta hakika", saboda daga Alkur'ani da Sunna ake dauko su.

Da wannan za ka san kuskuren 'Yan Kungiyar Salafiyyun, na kirkiran wasu abubuwa da sanya su matsayin "Usulus Salafiyya", kamar:
1- "Imtihani da Ashkhaas", wato yin jarabawa wa mutane da Shaikh wane, da wane.
2- Inkarin Muwazana.
3- Al- Jarhu wat Ta'adeel, da makamantansu.

Comments

Popular posts from this blog

Tarihin Sayyadina Umar bin Khaddab عمر بن الخطاب, (Allah Ya kara masa yarda):

Shimfiɗa.  Umar bn al-Khaṭṭāb ( RA) shi ne khalifan Rashidun na biyu, wanda ya yi mulki daga watan Agusta 634 har zuwa kashe shi a shekara ta 644. Ya gaji  Sayyidina Abubakar ( RA) a matsayin khalifan Rashidun na biyu a ranar 23 ga Agusta 634. Umar babban sahabi ne kuma surukinsa annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama. Menene Umar Ibn al-Khattab aka sani da shi? Umar babban sahabi ne kuma mashawarcin annabin musulunci Muhammad SAW, kuma ya zama shugaba musulmi na biyu bayan wafatin Muhammad ya kuma yi mulki na tsawon shekaru 10. Ya Musulunta a shekara ta 6 bayan wahayin Annabi Muhammadu Sallallahu alaihi Wasallama na farko, ya shafe shekaru 18 yana sahabi Muhammad SAW.  “Da za a samu wani Annabi a bayana, da ya kasance Umar dan Khaddabi ne.”  – Manzon Allah (SAW). Shi ne Umar dan Khaddabi dan Nufailu dan Addi dan Abdul Uzza dan Ribalu dan Abdullahi dan Kurdu dan Razahu dan Addi dan Ka’abu, Bakuraishe, Bamakhzume. Sun hada nasaba da Annabi (SAW). Ana yi masa alku...

MAGANIN KARYA SIHIRI(HAYAKI)

 Alhamdulillah kamar yadda mukai Alkawarin zamu kawo maganin wanda yake karya sihiri ko jifa,ko sammu Allah ya nufa yau mun cika shi. Kuma shi wannan na hayaki ne wanda mutum zai hada ya rika zuba shi akan garwashi yana amfami dashi,yadda abun yake kuma shine..... ABINDA ZAA NEMA. 1. Kaikayi koma kan mashekiya 2. Garin kusdul hindi 3. Garin haltit Zaa hade wannan waje daya,sai a rika diban kadan ana zubawa akan wuta mara lafiya ya rika shakar hayakin. Idan kuma don kariya zaai kawai sai a saka a daki ko a cikin gida. Wallahu a'alamu Abin sadaqa ayiwa Annabi sallallahu Alaihi wasallam Salati. LIKE AND SHARE.

SAHABBAI GOMA DA AKA YIWA BUSHARA DA ALJANNA TIN ANAN DUNIYA:-

 *1. Abubakar As-sidiq(R.A) *2. Umar Bin Khattab(R.A) *3. Uthman Bin Affan(R.A) *4. Aliyu Bin Abi-Talib(R.A) *5. Zubair Bin Auwam(R.) *6. Sa'adu Bin Abi Waqas(R.A) *7. Abu Ubaida Bin Jarrah(R.A) *8. Dalhatu Bin Ubaidullah(R.A) *9. Abdurrahman Bin Auf(R.A) *10. Sa'idu Bin Zaid Al-Quraishi(R.A). ♡♡♤♤♡♡♤♤♡♡ ALLAH YA BAMU ALBARKACINSU, ALLAH YA KARA LINKA RAHAMA DA YARDA A GARE SU AMEEEEEN.