Skip to main content

Posts

Showing posts from December, 2019

Shin ko kasan yanda Muqabalar Alkali Abubakar Al-Baqillaniy a kan Annabi Isa (as) a Fadar Paparoma ta Gudana?

Paparoma ya ji Fada ya nuna akwai matsala a cikin maruwaitar Mu'ujizar tsagewar wata ga Annabi Muhammad (saw), har ya ji dadi, ya samu kofar sukar Mu'ijizar Annabi (saw), shi ya sa ya tambayi Fadan, ta yaya za a soki maruwaita Mu'ijizar ta tsagewar wata? Sai Fada ya ce: Irin wadannan Mu'ujizozi in da a ce sun inganta, to dole a ce mutane masu yawa ne suka ruwaito daga wasu mutanen masu yawa, haka har ya iso gare mu. Da a ce haka ya faru da dole mu san hakan ya faru. Amma tun da hakan bai faru ba, to wannan yana nuna cewa; kawai karya ce aka kirkira. Sai Paparoma ya juya ya fiskanci Alkali Abubakar Al-Baqillaniy, ya ce: To kawo amsa. Sai Alkali Abubakar Al-Baqillaniy ya ce: To ai abin da kuka fada a kan tsagewar watan irinsa zan fada a kan "Ma'ida" da aka saukar wa Annabi Isa (as) daga sama. Sai a ce muku: Da a ce da gaske an saukar wa Annabi Isa (as) "Ma'ida" daga sama to dole a ce mutane masu yawa ne suka ruwaito daga wasu mutanen su...

SHIN KASAN BABU ABIN DA YAKE KAWO SABANI NA RABUWAR KAI KAMAR JAHILCI DA ZALUNCI DA MUMMUNAN NUFI

Lallai sabuba da dalilai da suke kaiwa ga mummunan sabani wanda Allah da Manzonsa (saw) suka yi zargi a kansa, kuma Allah ya tanadi azaba a kansa, wanda yake raba kan al'umma suna da yawa, amma mafi girmansu shi ne JAHILCI da BACIN NIYYA DA MUNGUN NUFI, wanda ya kunshi kulla zalunci da hasada a cikin zuciya da son neman daukaka a bayan kasa. Wannan shi ne sababin da ya sa Yahudawa suka yi sabani da rarrabuwa a tsakaninsu, kuma Allah ya zargesu a dalilin haka. Allah ya ce: ولقد آتينا بني إسرائيل الكتاب والحكم والنبوة ورزقناهم من الطيبات وفضلناهم على العالمين (16) وآتيناهم بينات من الأمر فما اختلفوا إلا من بعد ما جاءهم العلم بغيا بينهم إن ربك يقضي بينهم يوم القيامة فيما كانوا فيه يختلفون (17) Shaikhul Islam Ibnu Taimiyyah (r) ya ce: الاختلاف المذموم من الطرفين يكون سببه تارة: فساد النية؛ لما في النفوس من البغي والحسد وإرادة العلو في الأرض ونحو ذلك، فيحب لذلك ذم قول غيرها، أو فعله، أو غلبته ليتميز عليه، أو يحب قول من يوافقه في نسب أو مذهب أو بلد أو صداقة، ونحو ذلك، لما في قيام قوله من...

Son Zuciya Ne Kirkirar Masarautu!!! Daurawa Yayi Ganduje Raddi Me Zafi A...